Domin Kira Zuwa ga Addinin Musulunci da Raddi ga Miyagun Aƙidu Telegram ⚪⚪⚪⚪⚪⚪⚪⚪ *ZAƁAƁƁUN HADISAN ANNABI (S.A.W)* *HADISI NA 9* عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ أَنَّ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ : " رُبَّ أَشْعَثَ مَدْفُوعٍ بِالْأَبْوَابِ، لَوْ أَقْسَمَ عَلَى اللَّهِ لَأَبَرَّهُ ". FASSARA An karɓo daga Abu Hurairah (R.A). Haƙiƙa Manzon Allah (S.A.W) ya ce: "Duk wanda ya kasance; gashinsa ya duddunƙule (saboda rashin wanka), jikinsa ya yi kaca-kaca (saboda tsabar talauci), wanda idan ya yi sallama za a tsayar da shi a bakin ƙofa (saboda tsabar talaucinsa): da zai yi rantsuwa ga Allah (kan wani abu), tabbas da sai Allah ya kuɓutar da shi!" Muslim ne ya rawaito DARASI - Allah (S.W.T) ba ruwansa da dukiya ko kuɗi da ɗan adam ya mallaka, Allah ya fi ƙaunar zuciya mai taƙawa da ayyuka na ƙwarai. - Duk wanda ya ke da taƙawa ga Allah (S.W.T) ko da a ce shi ya fi kowa talauci a garinsu, da zai roƙi Allah wani abu, tabbas sai Allah ya amsa masa, saboda ku...
Nana Khadija(R.A) ga kyau, ga kudi,ga ilimi,ga kasuwanci, ga dangi gami da kaifin hankali da hangen Nesa. Zaku Iya Kallon Mu Da Bibiyar Ta Wadannan Kafofi kamar Haka YouTube , Facebook , And WhatsApp Khudubar Sallar Juma'a Mai Taken Biyayya Ga Mahaifa Tare Da Sheikh Adam Mahmud Sharada Ku Ziyarci Shafin Mu Na YouTube
Ana bude 'kofofin sama a kullum a dai dai lokacin Azahar domin masu addu'o'i da Neman biyan bukata!!! _____________________ ~ "Sallolin Nafila raka'o'i hudu kafin sallar Azahar suna bude wa mutum kofofin sama, wanda yayi wadannan salloli raka'o'i hudu kafin Azahar dai dai yake da wanda yayi salloli acikin dare a tsakiyar dare". 🎤: Inji Manzon Allah (S.A.W). Karanta "Sil-silah Sahiha" - Hadisi na 1,431. Wasu mutane sun tambayi Manzon Allah me yasa yake yin raka'o'i hudu kafin sallar Azahar, sai Manzon Allah yace "Saboda a lokacin Allah yake bada umarni a bude kofofin sama, akan shigar da aiyukan alkhairin zuwa gare shi". ~ Karanta Sunanu Abu Dawud, hadisi na 3,128. Nana Aisha (R.A) tace "Manzon Allah ya kasance yakan yi sallolin Nafila raka'o'i hudu bayan sallar Azahar idan bai samu damar yi ba kafin sallar Azahar din". Karanta Sunanut Tirmiziy, hadisi na 426. ~ Wani mutum ya tambayi Manzon...
Comments
Post a Comment